Muslim Library

Surah Ad-Dukhan ( The Smoke )

Select reciter

Hausa

Surah Ad-Dukhan ( The Smoke ) - Aya count 59
Facebook Twitter Google+ Pinterest Reddit StumbleUpon Linkedin Tumblr Google Bookmarks Email
حم ( 1 ) Ad-Dukhan ( The Smoke ) - Aya 1
Ḥ. M̃.
وَالْكِتَابِ الْمُبِينِ ( 2 ) Ad-Dukhan ( The Smoke ) - Aya 2
Inã rantsuwa da Littãfi Mabayyani.
إِنَّا أَنزَلْنَاهُ فِي لَيْلَةٍ مُّبَارَكَةٍ ۚ إِنَّا كُنَّا مُنذِرِينَ ( 3 ) Ad-Dukhan ( The Smoke ) - Aya 3
Lalle ne, Mũ, Muka saukar da shi a cikin wani dare mai albarka. Lalle Mũ' Mun kasance Mãsu yin gargaɗi.
فِيهَا يُفْرَقُ كُلُّ أَمْرٍ حَكِيمٍ ( 4 ) Ad-Dukhan ( The Smoke ) - Aya 4
A cikinsa (shi daren) ake rarrabe kõwane umurui bayyananne.
أَمْرًا مِّنْ عِندِنَا ۚ إِنَّا كُنَّا مُرْسِلِينَ ( 5 ) Ad-Dukhan ( The Smoke ) - Aya 5
Umurni na daga wurinMu. Lalle Mũ ne Muka kasanceMãsu aikãwã.
رَحْمَةً مِّن رَّبِّكَ ۚ إِنَّهُ هُوَ السَّمِيعُ الْعَلِيمُ ( 6 ) Ad-Dukhan ( The Smoke ) - Aya 6
Sabõda rahama daga Ubangijinka. Lalle Shĩ, Shi ne Mai ji, Mãsani.
رَبِّ السَّمَاوَاتِ وَالْأَرْضِ وَمَا بَيْنَهُمَا ۖ إِن كُنتُم مُّوقِنِينَ ( 7 ) Ad-Dukhan ( The Smoke ) - Aya 7
(Shĩ ne) Ubangijin sammai da ƙasa da abin da ke a tsakãninsu, idan kun kasance mãsu yaƙĩni (za ku gãne haka).
لَا إِلَٰهَ إِلَّا هُوَ يُحْيِي وَيُمِيتُ ۖ رَبُّكُمْ وَرَبُّ آبَائِكُمُ الْأَوَّلِينَ ( 8 ) Ad-Dukhan ( The Smoke ) - Aya 8
Babu abin bautãwa fãce Shi. Yana rãyarwa Kuma Yana kashẽwa. (Shi ne) Ubangijinku, kuma Ubangijin ubanninku na farko.
بَلْ هُمْ فِي شَكٍّ يَلْعَبُونَ ( 9 ) Ad-Dukhan ( The Smoke ) - Aya 9
A'a sũ, sunã wãsã a cikin shakka.
فَارْتَقِبْ يَوْمَ تَأْتِي السَّمَاءُ بِدُخَانٍ مُّبِينٍ ( 10 ) Ad-Dukhan ( The Smoke ) - Aya 10
Sabõda haka, ka dakata rãnar da sama zã tã zo da hayãƙi bayyananne.
يَغْشَى النَّاسَ ۖ هَٰذَا عَذَابٌ أَلِيمٌ ( 11 ) Ad-Dukhan ( The Smoke ) - Aya 11
Yanã rufe mutãne. Wannan wata azãba ce mai raɗaɗi.
رَّبَّنَا اكْشِفْ عَنَّا الْعَذَابَ إِنَّا مُؤْمِنُونَ ( 12 ) Ad-Dukhan ( The Smoke ) - Aya 12
Ya Ubangijinmu! Ka kuranye mana azãba. Lalle Mũ, mãsu ĩmãni ne.
أَنَّىٰ لَهُمُ الذِّكْرَىٰ وَقَدْ جَاءَهُمْ رَسُولٌ مُّبِينٌ ( 13 ) Ad-Dukhan ( The Smoke ) - Aya 13
Inã tunãwa take a gare su, alhãli kuwa, haƙĩƙa, Manzo mai bayyanãwa Ya je musu (da gargaɗin saukar azãbar, ba su karɓa ba)?
ثُمَّ تَوَلَّوْا عَنْهُ وَقَالُوا مُعَلَّمٌ مَّجْنُونٌ ( 14 ) Ad-Dukhan ( The Smoke ) - Aya 14
Sa'an nan suka jũya baya daga gare shi, Kuma suka ce: "Wanda ake gayãwa ne, mahaukaci."
إِنَّا كَاشِفُو الْعَذَابِ قَلِيلًا ۚ إِنَّكُمْ عَائِدُونَ ( 15 ) Ad-Dukhan ( The Smoke ) - Aya 15
Lalle Mũ, Mãsu kuranyẽwar azãba ne, a ɗan lõkaci kaɗan, lalle kũ, mãsu kõmãwa ne (ga laifin).
يَوْمَ نَبْطِشُ الْبَطْشَةَ الْكُبْرَىٰ إِنَّا مُنتَقِمُونَ ( 16 ) Ad-Dukhan ( The Smoke ) - Aya 16
Rãnar da Muke damƙa, damƙa mafi girma, lalle ne Mũ mãsu azãbar rãmuwa ne.
وَلَقَدْ فَتَنَّا قَبْلَهُمْ قَوْمَ فِرْعَوْنَ وَجَاءَهُمْ رَسُولٌ كَرِيمٌ ( 17 ) Ad-Dukhan ( The Smoke ) - Aya 17
Kuma lalle ne haƙĩƙa a gabaninsu, Mun fitini mutãnen Fir'auna, kuma wani Manzo karĩmi ya jẽ musu.
أَنْ أَدُّوا إِلَيَّ عِبَادَ اللَّهِ ۖ إِنِّي لَكُمْ رَسُولٌ أَمِينٌ ( 18 ) Ad-Dukhan ( The Smoke ) - Aya 18
(Mazon ya ce): "Ku kãwo mini (ĩmãninku) ya bayin Allah! Lalle ni, Manzo ne amintacce zuwa gare ku."
وَأَن لَّا تَعْلُوا عَلَى اللَّهِ ۖ إِنِّي آتِيكُم بِسُلْطَانٍ مُّبِينٍ ( 19 ) Ad-Dukhan ( The Smoke ) - Aya 19
"Kuma kada ku nẽmi ɗaukaka a kan Allah. Lalle nĩ mai zo muku ne da dalĩli bayyananne."
وَإِنِّي عُذْتُ بِرَبِّي وَرَبِّكُمْ أَن تَرْجُمُونِ ( 20 ) Ad-Dukhan ( The Smoke ) - Aya 20
"Kuma lalle nĩ na nẽmi tsari da Ubangijĩna, kuma Ubangijinku, dõmin kada ku jẽfe ni."
وَإِن لَّمْ تُؤْمِنُوا لِي فَاعْتَزِلُونِ ( 21 ) Ad-Dukhan ( The Smoke ) - Aya 21
"Kuma idan ba ku yi ĩmãni sabõda nĩ ba, to, ku nĩsance ni."
فَدَعَا رَبَّهُ أَنَّ هَٰؤُلَاءِ قَوْمٌ مُّجْرِمُونَ ( 22 ) Ad-Dukhan ( The Smoke ) - Aya 22
Sai ya kirayi Ubangjinsa cẽwa waɗannan mutãnene mãsu laifi.
فَأَسْرِ بِعِبَادِي لَيْلًا إِنَّكُم مُّتَّبَعُونَ ( 23 ) Ad-Dukhan ( The Smoke ) - Aya 23
(Allah Ya ce): "To, ka yi tafiyar dare da bayiNa, da dare. Lalle kũ, waɗanda ake bĩ ne (dõmin a kãma ku.)"
وَاتْرُكِ الْبَحْرَ رَهْوًا ۖ إِنَّهُمْ جُندٌ مُّغْرَقُونَ ( 24 ) Ad-Dukhan ( The Smoke ) - Aya 24
"Kuma ka bar tẽku rarrabe. Lalle sũ, runduna ce abar nutsarwa."
كَمْ تَرَكُوا مِن جَنَّاتٍ وَعُيُونٍ ( 25 ) Ad-Dukhan ( The Smoke ) - Aya 25
Da yawa suka bar gõnaki da marẽmari.
وَزُرُوعٍ وَمَقَامٍ كَرِيمٍ ( 26 ) Ad-Dukhan ( The Smoke ) - Aya 26
Da shuke-shuke da matsayi mai kyau.
وَنَعْمَةٍ كَانُوا فِيهَا فَاكِهِينَ ( 27 ) Ad-Dukhan ( The Smoke ) - Aya 27
Da wata ni'ima da suka kasance a cikinta sunã mãsu hutu.
كَذَٰلِكَ ۖ وَأَوْرَثْنَاهَا قَوْمًا آخَرِينَ ( 28 ) Ad-Dukhan ( The Smoke ) - Aya 28
Kamar haka! Kuma Muka gãdar da ita ga waɗansu mutãne na dabam.
فَمَا بَكَتْ عَلَيْهِمُ السَّمَاءُ وَالْأَرْضُ وَمَا كَانُوا مُنظَرِينَ ( 29 ) Ad-Dukhan ( The Smoke ) - Aya 29
Sa'an nan samã da ƙasã ba su yi kũka a kansu ba, Kuma ba su kasance waɗanda ake yi wa jinkiri ba.
وَلَقَدْ نَجَّيْنَا بَنِي إِسْرَائِيلَ مِنَ الْعَذَابِ الْمُهِينِ ( 30 ) Ad-Dukhan ( The Smoke ) - Aya 30
Kuma lalle ne, haƙĩƙa Mun tsĩrar da Banĩ Isrã'ĩla daga, azãba mai wulãkantãwa.
مِن فِرْعَوْنَ ۚ إِنَّهُ كَانَ عَالِيًا مِّنَ الْمُسْرِفِينَ ( 31 ) Ad-Dukhan ( The Smoke ) - Aya 31
Daga Fir'auna. Lalle shi, ya kasance maɗaukaki daga cikin mãsu ɓarna.
وَلَقَدِ اخْتَرْنَاهُمْ عَلَىٰ عِلْمٍ عَلَى الْعَالَمِينَ ( 32 ) Ad-Dukhan ( The Smoke ) - Aya 32
Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun zãɓe su sabõda wani ilmi (na Taurata) a kan mutãne.
وَآتَيْنَاهُم مِّنَ الْآيَاتِ مَا فِيهِ بَلَاءٌ مُّبِينٌ ( 33 ) Ad-Dukhan ( The Smoke ) - Aya 33
Kuma Muka bã su, daga ãyõyin mu'ujizõji, abin da yake a cikinsa, akwai ni'ima bayyananna
إِنَّ هَٰؤُلَاءِ لَيَقُولُونَ ( 34 ) Ad-Dukhan ( The Smoke ) - Aya 34
Lalle waɗannan mutãne, haƙĩka, sunã cẽwa,
إِنْ هِيَ إِلَّا مَوْتَتُنَا الْأُولَىٰ وَمَا نَحْنُ بِمُنشَرِينَ ( 35 ) Ad-Dukhan ( The Smoke ) - Aya 35
"Babu wani abu sai mutuwarmu ta farko, kuma ba mu zama waɗanda ake tãyarwa ba."
فَأْتُوا بِآبَائِنَا إِن كُنتُمْ صَادِقِينَ ( 36 ) Ad-Dukhan ( The Smoke ) - Aya 36
"Sai ku zo da ubanninmu, idan kun kasance mãsu gaskiya."
أَهُمْ خَيْرٌ أَمْ قَوْمُ تُبَّعٍ وَالَّذِينَ مِن قَبْلِهِمْ ۚ أَهْلَكْنَاهُمْ ۖ إِنَّهُمْ كَانُوا مُجْرِمِينَ ( 37 ) Ad-Dukhan ( The Smoke ) - Aya 37
shin, sũ ne mafĩfĩta kõ kuwa mutãnen Tubba'u, kuma da waɗanda ke a gabãninsu? Mun halaka su, lalle sũ, sun kasance mãsu laifi.
وَمَا خَلَقْنَا السَّمَاوَاتِ وَالْأَرْضَ وَمَا بَيْنَهُمَا لَاعِبِينَ ( 38 ) Ad-Dukhan ( The Smoke ) - Aya 38
Kuma ba Mu halitta slmmai da ƙasa da abin da ke a tsakãninsu ba, alhãli kuwa Munã mãsu wãsã.
مَا خَلَقْنَاهُمَا إِلَّا بِالْحَقِّ وَلَٰكِنَّ أَكْثَرَهُمْ لَا يَعْلَمُونَ ( 39 ) Ad-Dukhan ( The Smoke ) - Aya 39
Ba Mu halitta su ba fãce da manufa ta gaskiya, kuma amma mafi yawansu, ba su sani ba.
إِنَّ يَوْمَ الْفَصْلِ مِيقَاتُهُمْ أَجْمَعِينَ ( 40 ) Ad-Dukhan ( The Smoke ) - Aya 40
Lalle rãnar rarrabẽwa, ita ce lõkacin wa'adinsu gabã ɗaya.
يَوْمَ لَا يُغْنِي مَوْلًى عَن مَّوْلًى شَيْئًا وَلَا هُمْ يُنصَرُونَ ( 41 ) Ad-Dukhan ( The Smoke ) - Aya 41
Rãnar da wani zumu bã ya amfãnin wani zumu da kõme kuma ba su zama anã taimakon su ba.
إِلَّا مَن رَّحِمَ اللَّهُ ۚ إِنَّهُ هُوَ الْعَزِيزُ الرَّحِيمُ ( 42 ) Ad-Dukhan ( The Smoke ) - Aya 42
fãce wanda Allah Ya yi wa rahama. Lalle Shi (Allah), shĩ ne Mabuwãyi, Mai jin ƙai.
إِنَّ شَجَرَتَ الزَّقُّومِ ( 43 ) Ad-Dukhan ( The Smoke ) - Aya 43
Lalle itãciyar zaƙƙũm (ɗanyen wutã),
طَعَامُ الْأَثِيمِ ( 44 ) Ad-Dukhan ( The Smoke ) - Aya 44
Ita ce abincin mai laifi.
كَالْمُهْلِ يَغْلِي فِي الْبُطُونِ ( 45 ) Ad-Dukhan ( The Smoke ) - Aya 45
Kamar narkakken kwalta yanã tafasa a cikin cikunna.
كَغَلْيِ الْحَمِيمِ ( 46 ) Ad-Dukhan ( The Smoke ) - Aya 46
Kamar tafasar ruwan zãfi.
خُذُوهُ فَاعْتِلُوهُ إِلَىٰ سَوَاءِ الْجَحِيمِ ( 47 ) Ad-Dukhan ( The Smoke ) - Aya 47
(A cẽ wa malã'ikun wutã), "Ku kãmã shi, sa'an nan ku fizge shi zuwa ga tsakiyar Jahĩm."
ثُمَّ صُبُّوا فَوْقَ رَأْسِهِ مِنْ عَذَابِ الْحَمِيمِ ( 48 ) Ad-Dukhan ( The Smoke ) - Aya 48
"Sa'an nan ku zuba, a kansa, daga azãbar ruwan zãfi."
ذُقْ إِنَّكَ أَنتَ الْعَزِيزُ الْكَرِيمُ ( 49 ) Ad-Dukhan ( The Smoke ) - Aya 49
(A ce masã), "Ka ɗanɗana! Lalle kai, kai ne mabuwãyi mai girma!"
إِنَّ هَٰذَا مَا كُنتُم بِهِ تَمْتَرُونَ ( 50 ) Ad-Dukhan ( The Smoke ) - Aya 50
"Lalle wannan, shi ne abin da kuka kasance kunã shakka game da shi."
إِنَّ الْمُتَّقِينَ فِي مَقَامٍ أَمِينٍ ( 51 ) Ad-Dukhan ( The Smoke ) - Aya 51
Lalle mãsu taƙawa sunã cikin matsayi amintacce.
فِي جَنَّاتٍ وَعُيُونٍ ( 52 ) Ad-Dukhan ( The Smoke ) - Aya 52
A cikin gidãjen Aljanna da marẽmari.
يَلْبَسُونَ مِن سُندُسٍ وَإِسْتَبْرَقٍ مُّتَقَابِلِينَ ( 53 ) Ad-Dukhan ( The Smoke ) - Aya 53
Sunã tufanta daga tufãfin alharĩni raƙĩƙi, da mai kauri, sunã mãsu zaman fuskantar jũna.
كَذَٰلِكَ وَزَوَّجْنَاهُم بِحُورٍ عِينٍ ( 54 ) Ad-Dukhan ( The Smoke ) - Aya 54
Kamar haka, kuma Mun aurar da su da mãtã mãsu kyaun idãnu, mãsu girmansu.
يَدْعُونَ فِيهَا بِكُلِّ فَاكِهَةٍ آمِنِينَ ( 55 ) Ad-Dukhan ( The Smoke ) - Aya 55
Sunã kira, a cikinsu (gidẽjen) ga dukan 'ya'yan itãcen marmari, sunã amintattu (daga dukan abin tsõro).
لَا يَذُوقُونَ فِيهَا الْمَوْتَ إِلَّا الْمَوْتَةَ الْأُولَىٰ ۖ وَوَقَاهُمْ عَذَابَ الْجَحِيمِ ( 56 ) Ad-Dukhan ( The Smoke ) - Aya 56
Bã su ɗanɗanar mutuwa, a cikinsu, fãce mutuwar farko, kuma (Allah), Ya tsare musu azãbar Jahĩm.
فَضْلًا مِّن رَّبِّكَ ۚ ذَٰلِكَ هُوَ الْفَوْزُ الْعَظِيمُ ( 57 ) Ad-Dukhan ( The Smoke ) - Aya 57
Sabõda falala daga Ubangijinka. Wancan shi ne babban rabo, mai girma.
فَإِنَّمَا يَسَّرْنَاهُ بِلِسَانِكَ لَعَلَّهُمْ يَتَذَكَّرُونَ ( 58 ) Ad-Dukhan ( The Smoke ) - Aya 58
Dõmin haka kawai Muka sauƙaƙar da shi (Alƙur'ãni) da harshenka, tsammãninsu, su riƙa tunãwa.
فَارْتَقِبْ إِنَّهُم مُّرْتَقِبُونَ ( 59 ) Ad-Dukhan ( The Smoke ) - Aya 59
Sai ka yi jira. Lalle sũ, mãsu jira ne.
Facebook Twitter Google+ Pinterest Reddit StumbleUpon Linkedin Tumblr Google Bookmarks Email

Select language

Select surah